Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, a Benin, ta kama Irabor Kennedy Osasogie, bisa zargin zamba bayan wata kara da Antje, dan kasar Jamus ya shigar.
Matar ta kai karar hukumar cewa Osasogie, mai shekaru 21, ya damfare ta kudi Yuro 17,000.
Mai shigar da karar ta yi ikirarin cewa ta hadu da shi ta kafafen sada zumunta bayan da wani Michael Patrick ya damfare ta kudi Yuro 68,000.
Antje ta yi zargin cewa Osasogie ya nemi ya taimaka mata wajen kwato kudin amma ya ci gaba da damfarar ta Yuro 17,000.
Wata sanarwa da mai magana da yawun EFCC, Wilson Uwujaren ya fitar ta ce bayan kama shi, wanda ake zargin ya ce ya samu Yuro 12,850 ne kawai.
Uwujaren ya kara da cewa “Za a gurfanar da wanda ake zargin zuwa kotu da zarar an kammala bincike.”