Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) ta gurfanar da Kakakin majalisar dokokin jihar Ondo, Bamidele Oleyelogun, a gaban babban kotun jiha da ke zamanta a cikin gidan ajiya da gyaran hali na Olokuta da ke Akure babban birnin jihar bisa zarge-zargen badakala.
An dai gurfanar da Oleyelogun tare da wasu mambobin majalisar dokokin, bisa zargin badakalar kudin shirya wani taron bita da yawan kudin ya kai Naira miliyan 2.4.
Jaridar Leadership ta rawaito cewa, a yayin zaman kotun, an samu rashin jituwa tsakanin jami’an gidan ajiya da gyaran hali da ‘yan jarida a lokacin da masu kula da gidan suka hana ‘yan jarida su shiga domin sauraron yadda shari’ar ke wakana.
Gandirobobin a karkashin jagorancin kwamandan gidan ajiya da gyaran hali, Ibrahim Ayooola Ogunja, sun ce sun samu umarni daga wajen Kwantirola da ke kula da gidan ajiya da gyaran halin na su na hana ‘yan jaridan shiga cikin farfajiyar gidan.