Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ta gabatar da sabbin tuhume-tuhume 17 a kan tsohon gwamnan jihar Imo kuma Sanata mai wakiltar mazabar Imo ta Yamma.
A tuhumar da ta gabatar a gaban wata babbar kotun tarayya a Abuja, EFCC ta ce, Rochas ya hada baki da wasu, wadanda suka hada da ‘yan jam’iyyar APC, da wasu kamfanoni biyar suka saci Naira biliyan 2.9 daga asusun gwamnati.
Hukumar ta dauki wannan mataki ne sa’o’i bayan da toshon gwamnan ya kaddamar da aniyarsa ta takarar shugaban kasa a Najeriyar a 2023.
A watan Afrilu na 2021, EFCC ta kama Okorocha, ta tsare shi har tsawonkwana biyu tana yi wa toshon gwamnan wanda ya mulki jihar Imo daga 2011 zuwa 2019 tambayoyi a kan batutuwn da suka shafi zargin cin hanci. In ji BBC.
Gwamnatin jihar ta yanzu tana zarginsa da aikata laifukan cin hanci da rashawa da almundahana da dama, sai dai kuma ya musanta dukkanin zarge-zargen.