fidelitybank

Duk rintsi za mu zauna a ƙasar mu – Falasɗinawa

Date:

Shugabannin ƙasashen yankin Gabas ta Tsakiya da na Turai sun gudanar da wani taro a birnin Alƙahira na ƙasar Masar, domin tattauna batun rikicin Isra’ila da Gaza.

Yayin da yake jawabi a wajen taron, shugaban Falasɗinawa Mahmoud Abbas, ya ce babu wanda zai tilasta wa Falasɗinawa barin ƙasarsu.

“Ba za mu amince da ficewa daga ƙasarmu ba, za mu ci gaba da zama a ƙasarmu, a kowane hali kuwa”, in ji shi.

Mahmoud Abbas shi ne shugaban gwamnatin Falsɗinawa, da ke da iko da yankunan Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da aka mamaye, to amma ba ya iko da yankin Zirin Gaza.

A baya ƙasar Masar da sauran ƙasashen Larabawa sun ce ba za a amince da kwararar Falasɗinawa domin zama ‘yan gudun hijira ba, saboda a cewarsu hakan zai tilasta fitar da su daga ƙasarsu.

Taron wanda aka yi wa laƙabi da ‘Taron Zaman Lafiya’ ya ƙunshi wakilai daga ƙasashen Jordan da Qatar da Italiya da Sifaniya da Tarayar Turai da Birtaniya.

Sai dai ba a ga wakilan ƙasashen Amurka da Isra’ila da Iran a wajen taron ba.

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp