fidelitybank

Duk lokacin da na ga Abba ya dauka a kan layi zan a ƙarar da shi – Kwankwaso

Date:

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a zaɓen da ya wuce, Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ce ba zai yi wa gwamnan Kano mai jiran gado, Abba Kabir Yusuf, katsalandan cikin harkokin mulkinsa ba.

Kwankwaso, wanda shi ne jagoran NNPP na ƙasa, kuma wanda ake gani a matsayin ubangidan Abba Gida-Gida a siyasance, ya ce idan gwamnan mai jiran gado ya nemi shawararsa, zai ba shi.

Karanta Wannan: Ƴan Sanda sun kaddamar da yaƙi da miyagun ƙwayoyi da ƴan Dana a Kano

Wasu mutane sun yi ta nuna fargabar cewa ba lallai ne Abba Kabir Yusuf ya samu cikakken ikon tafiyar da gwamnatin Kano ba, idan an rantsar da shi, saboda mai yiwuwa Kwankwaso zai yi ta ba shi umarni da yi masa katsalandan.

Sai dai, yaayin wata hira da BBC, tsohon gwamnan na Kano, ya ce a matsayinsa na ɗan Kano zai riƙa ankarar da gwamnatin wadda za a rantsar a ƙarshen watan Mayu, duk lokacin da ya ga ta kauce hanya.

Ya ce “Ai shi mulki ko mai shararka ne, ka ba shi, to ka koma waje ɗaya in ya nemi shawararka ka bayar, idan kuwa bai nema ba, sai ka yi shiru.”

abin da ya sani, in ji Kwankwaso, shi ne a lokacin da yake gwamna a Kano, da su Abba aka yi mulkin, su ne suka taimaka ya cimma nasarar da ya samu.

Kwankwaso ya ce, “ A yanzu na tabbata abun da Ganduje ya yi a Kano, ai Abba ya wuce wannan.

Saboda haka ne ma, muka zauna muka duba dukkan mutanen namu muka ɗauki wanda muke ganin idan Allah ya yarda in dai irin matsaloli na Ganduje ne ba za a samu ba.”

Tsohon gwamnan, ya ce,” Dukkanninmu a jihar Kano muna farin ciki Allah ya fitar da su, kuma muna addu’ar Allah ya raka taki gona.”

A cewar Kwankwaso, abin da yake so a sani shi ne ”ko wane ne yake mulkin Kano, ko soja ko ma wane ne, to ba za mu kyale shi, ya yi rashin kyautawa ba.”

“Don haka ko Abba ne ke mulki ko ma waye duk wani abu da yake daidai za mu faɗa masa, idan ma ba daidai ba ne za mu faɗa.”

Kwankwaso ya ce, shi abin da ya sani, shi ne za a gyara duk wasu abubuwa da aka yi ba daidai ba, a lokacin gwamnati mai barin gado.

Ya kuma ce, za su yi hakan ne don a gyara Kano ta yi kyau.

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...
X whatsapp