Duk da gargadin da shugaban kungiyar ECOWAS, Bola Tinubu ya yi a ranar Larabar da ta gabata, sojojin Nijar sun karbe ragamar mulki a safiyar Alhamis din nan daga hannun shugaba Mohamed Bazoum.
Shugaba Bazoum dai ya kasance a tsare tun da sanyin safiyar Laraba lokacin da sojoji suka fara yunkurin juyin mulkin.
Sojojin sun sanar da juyin mulkin ne a wani yaɗa shirye-shiryen da aka yi ta gidan talabijin da sanyin safiyar Alhamis.
Kimanin manyan hafsoshi 10 karkashin jagorancin Kanar Amadou Abdramane ne suka bayyana a yayin yaɗa shirye-shiryen cewa, majalisar tsaron kasar ta yanke shawarar kawo karshen mulkin da kuka saba da shi.
A cewarsu, ci gaban ya biyo bayan tabarbarewar tsaro a Nijar, da kuma rashin tafiyar da harkokin zamantakewa da tattalin arziki da gwamnati ke yi.
“Muna sake jaddada goyon bayanmu ga dukkan alkawuran da Nijar ta dauka,” in ji sojojin.
Kungiyar ta ECOWAS, ta bayyana hakan ne ta bakin shugabanta, Tinubu, ya yi Allah-wadai da yunkurin da aka yi tun farko, yana mai gargadin cewa kungiyar ta yankin, da ma sauran kasashen duniya, ba za su amince da kawo cikas ga kundin tsarin mulkin yankin ba.