fidelitybank

Duk da gargaɗin Tinubu Sojojin Nijar sun yi juyin mulki

Date:

Duk da gargadin da shugaban kungiyar ECOWAS, Bola Tinubu ya yi a ranar Larabar da ta gabata, sojojin Nijar sun karbe ragamar mulki a safiyar Alhamis din nan daga hannun shugaba Mohamed Bazoum.

Shugaba Bazoum dai ya kasance a tsare tun da sanyin safiyar Laraba lokacin da sojoji suka fara yunkurin juyin mulkin.

Sojojin sun sanar da juyin mulkin ne a wani yaɗa shirye-shiryen da aka yi ta gidan talabijin da sanyin safiyar Alhamis.

Kimanin manyan hafsoshi 10 karkashin jagorancin Kanar Amadou Abdramane ne suka bayyana a yayin yaɗa shirye-shiryen cewa, majalisar tsaron kasar ta yanke shawarar kawo karshen mulkin da kuka saba da shi.

A cewarsu, ci gaban ya biyo bayan tabarbarewar tsaro a Nijar, da kuma rashin tafiyar da harkokin zamantakewa da tattalin arziki da gwamnati ke yi.

“Muna sake jaddada goyon bayanmu ga dukkan alkawuran da Nijar ta dauka,” in ji sojojin.

Kungiyar ta ECOWAS, ta bayyana hakan ne ta bakin shugabanta, Tinubu, ya yi Allah-wadai da yunkurin da aka yi tun farko, yana mai gargadin cewa kungiyar ta yankin, da ma sauran kasashen duniya, ba za su amince da kawo cikas ga kundin tsarin mulkin yankin ba.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp