fidelitybank

Duban talakawa za su ci gaba da zaman gida saboda rufe makarantu – Mazauna Zamfara

Date:

Yayin da a ka koma makarantu a faɗin Najeriya a ranar Litinin, wasu iyayen yara a jihar Zamfara sun koka a kan rashin buɗe makarantun su.

Mazauna yankin sun ce rashin komawa makarantun ‘ya’yansu a safiyar yau, alama ce da ke nuna cewa dubban ‘ya’yan talakawa a jihar za su ci gaba da zaman gida tsawon zangon karatu na biyu ke nan.

Gwamnatin Zamfara dai ta rufe makarantun jihar ne a farkon watan Satumba, bayan sace gomman ɗalibai daga Sakandiren Ƙaya a cikin ƙaramar hukumar Muradun da yammacin ranar wata Laraba.

Wani mahaifi ya shaida wa BBC cewa suna tsaka mai wuya; ”Mu na kira ga gwamnatin jihar Zamfara ta duba girman Allah ta bude mana makarantun yara, wannan matsalar tsaro wadda ita ce a ka ce ta janyo rufe makarantun ba wai Zamfara kadai ta shafa ba, shin don me a nan za a mayar tamkar nan ne gidan matsalar”.

An yi zango guda yara na zaman gida, yanzu duk inda za a koma makaranta ban da namu ‘ya’yan. Kowancan Term guda da aka yi wasu daga cikin mutanenmu da sun san ba za a koma makarantar ba da tuni sun dauki mataki,” in ji shi.

An dai rufe makarantu tun watan Agustan bara, watanni biyar kenan, kuma babu wata magana guda har ya zuwa yanzu na bude makarantun.

 

 

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp