fidelitybank

Dole ne ku girbi abun da ku ka shuka – Tambuwal

Date:

Gwamnan Jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, ya yi Allah-wadai da harin da aka kai kan ayarin motocinsa a Sokoto tare da shan alwashin gurfanar da waɗanda suka kai harin a gaban kotu.

A wata sanarwa da mai bai wa gwamnan shawara kan harkokin watsa labarai Muhammad Bello ya fitar, wasu waɗanda ake kyautata zaton zauna garin banza ne suka yi ruwan duwatsu ga ayarin motocin gwamnan a cikin birnin Sokoto a lokacin da yake komawa birnin daga yaƙin neman zaɓen da yaje Ƙananan Hukumomin Wamakko da kuma Silame.

Cikin waɗanda suke cikin tawagar gwamnan a lokacin da aka kai harin har da ɗan takarar gwamna na PDP a Sokoto wato Mallam Saidu Umar da Janar Aminu Bande da mataimakin gwamnan Sokoto Honorabul Sagir Bafarawa, kuma dukansu babu wanda ya ji rauni kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Sai dai sanarwar ta ce akwai motoci biyu waɗanda aka lalata a lokacin harin.

A yayin wata hira da ƴan jarida, gwamnan Jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ya tabbatar da cewa an kama wasu daga cikin waɗanda suka kai harin kuma za a kai su kotu.

A wata hira ta daban da kwamishinan watsa labarai na jihar Honorabul Akibu Dalhatu ya yi da manema labarai, wanda ake zargi shi ne jagoran maharan wato wani Abu Mai Adda na daga cikin waɗanda hukumar tsaro ta farin kaya wato NSCDC ke nema ruwa a jallo kuma tuni aka kama shi.

Kwamishinan ya kuma ce ana zargin Mai Adda da lalata wasu motocin ayarin gwamnan da kuma sace babura biyar bayan kai hari ga magiya bayan PDP a lokacin yaƙin neman zaɓe a Wamakko.

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp