fidelitybank

Dole ne ku girbi abun da ku ka shuka – Tambuwal

Date:

Gwamnan Jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, ya yi Allah-wadai da harin da aka kai kan ayarin motocinsa a Sokoto tare da shan alwashin gurfanar da waɗanda suka kai harin a gaban kotu.

A wata sanarwa da mai bai wa gwamnan shawara kan harkokin watsa labarai Muhammad Bello ya fitar, wasu waɗanda ake kyautata zaton zauna garin banza ne suka yi ruwan duwatsu ga ayarin motocin gwamnan a cikin birnin Sokoto a lokacin da yake komawa birnin daga yaƙin neman zaɓen da yaje Ƙananan Hukumomin Wamakko da kuma Silame.

Cikin waɗanda suke cikin tawagar gwamnan a lokacin da aka kai harin har da ɗan takarar gwamna na PDP a Sokoto wato Mallam Saidu Umar da Janar Aminu Bande da mataimakin gwamnan Sokoto Honorabul Sagir Bafarawa, kuma dukansu babu wanda ya ji rauni kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Sai dai sanarwar ta ce akwai motoci biyu waɗanda aka lalata a lokacin harin.

A yayin wata hira da ƴan jarida, gwamnan Jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ya tabbatar da cewa an kama wasu daga cikin waɗanda suka kai harin kuma za a kai su kotu.

A wata hira ta daban da kwamishinan watsa labarai na jihar Honorabul Akibu Dalhatu ya yi da manema labarai, wanda ake zargi shi ne jagoran maharan wato wani Abu Mai Adda na daga cikin waɗanda hukumar tsaro ta farin kaya wato NSCDC ke nema ruwa a jallo kuma tuni aka kama shi.

Kwamishinan ya kuma ce ana zargin Mai Adda da lalata wasu motocin ayarin gwamnan da kuma sace babura biyar bayan kai hari ga magiya bayan PDP a lokacin yaƙin neman zaɓe a Wamakko.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...
X whatsapp