fidelitybank

Dole ne ku girbi abun da ku ka shuka – Tambuwal

Date:

Gwamnan Jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, ya yi Allah-wadai da harin da aka kai kan ayarin motocinsa a Sokoto tare da shan alwashin gurfanar da waɗanda suka kai harin a gaban kotu.

A wata sanarwa da mai bai wa gwamnan shawara kan harkokin watsa labarai Muhammad Bello ya fitar, wasu waɗanda ake kyautata zaton zauna garin banza ne suka yi ruwan duwatsu ga ayarin motocin gwamnan a cikin birnin Sokoto a lokacin da yake komawa birnin daga yaƙin neman zaɓen da yaje Ƙananan Hukumomin Wamakko da kuma Silame.

Cikin waɗanda suke cikin tawagar gwamnan a lokacin da aka kai harin har da ɗan takarar gwamna na PDP a Sokoto wato Mallam Saidu Umar da Janar Aminu Bande da mataimakin gwamnan Sokoto Honorabul Sagir Bafarawa, kuma dukansu babu wanda ya ji rauni kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Sai dai sanarwar ta ce akwai motoci biyu waɗanda aka lalata a lokacin harin.

A yayin wata hira da ƴan jarida, gwamnan Jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ya tabbatar da cewa an kama wasu daga cikin waɗanda suka kai harin kuma za a kai su kotu.

A wata hira ta daban da kwamishinan watsa labarai na jihar Honorabul Akibu Dalhatu ya yi da manema labarai, wanda ake zargi shi ne jagoran maharan wato wani Abu Mai Adda na daga cikin waɗanda hukumar tsaro ta farin kaya wato NSCDC ke nema ruwa a jallo kuma tuni aka kama shi.

Kwamishinan ya kuma ce ana zargin Mai Adda da lalata wasu motocin ayarin gwamnan da kuma sace babura biyar bayan kai hari ga magiya bayan PDP a lokacin yaƙin neman zaɓe a Wamakko.

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...

Ambaliyar ruwa ta kashe mutuane takwas a Ebonyi

Ambaliya, wadda mamakon ruwan sama ya janyo, ta yi...

Bankin Duniya zai kashe wa yankin Arewa a Najeriya dala miliyan 300

Bankin Duniya ya amince da kasafin kuɗi dala miliyan...

Giyar mulki na kwasar Trump – ‘Yan Majalisar Democrat

'Yan Democrats a Amurka sun zargi Donald Trump da...

Kama Aminu Waziri Tambuwal da EFCC ta yi ba daidai ba ne – PDP

Jam'iyyar PDP a jihar Sokoto ta yi Allah-wadai da...

An kai hari a ƙauyuka 15 na Zamfara a mako ɗaya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huɗu ne suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...
X whatsapp