fidelitybank

Dawo da Sunusi Sarkin Kano Kanzon Kurege ne – Majalisar Dokoki

Date:

Majalisar dokokin jihar Kano ta bayyana a matsayin wani hadadden labaran karya da aka ruwaito an yi yunkurin yin gyara ga dokar majalisar masarautun jihar da nufin dawowar tsohon sarki Muhammadu Sanusi II.

Majalisar ta kuma bayyana rade-radin cewa za su tsige sabbin sarakunan Gaya, Bichi, Rano, Karaye guda biyar domin baiwa hambararren Sarki Muhammadu Sanusi II damar samun cikakken iko a matsayin Sarkin Kano.

Kafofin sada zumunta sun yi kaca-kaca da labarin a ranar Larabar da ta gabata cewa Majalisar za ta sake duba batun masarautu, inda shugaban masu rinjaye, Lawan Hussaini, dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Dala, zai karanta daftarin dokar 2023 a ranar Alhamis, 15 ga watan Yuni. 2023.

An bayyana cewa an tsara shi ne majalisar ta tattauna batun tare da amincewa da gyaran da daga baya zai bada damar tsige sarakuna da kuma dawo da Khalifa Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano, tare da amincewar Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Da yake jawabi ga manema labarai a ranar Laraba bayan kammala zaman majalisar, shugaban masu rinjaye, Lawan Hussaini, ya bayyana labarin a matsayin labaran karya.

Hussaini ya ce babu wani yunkuri da zai sa ya karanta irin wannan gyara domin ba a taba tattauna batun ba.

‘’Abin ban dariya ne yayin da na karanta labaran karya kuma mutane da yawa suka tambaye ni ko ina sane da irin wannan shirin,’’ in ji dan majalisar.

Ya ce bayan majalisar ta amince da bukatar gwamnan na nadin masu ba shi shawara na musamman guda 20, ta dage zaman zuwa ranar Litinin 19 ga watan Yuni, 2023.

Shugaban masu rinjaye ya ce masu yada irin wadannan jita-jita mutane ne da ba sa son zaman lafiya a jihar

uanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp