fidelitybank

Dangote ya rage man fetur lita 840

Date:

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur daga naira 880 zuwa naira 840 ga dillalan da ke siyan man daga matatarsa, a wani mataki da ya zo gabanin fara rabon man a faɗin ƙasa daga 15 ga watan Agusta.

Shugaban hulɗa da jama’a na matatar, Anthony Chiejina, ne ya bayyana hakan, yana mai cewa rage farashin ya biyo bayan faɗuwar farashin danyen mai a kasuwannin duniya.

A baya-bayan nan, kamfanin man Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin fetur zuwa naira 925 a wasu tashoshinsa a Legas, daga naira 915.

Dangote ya ce sun sayi motoci 4,000 masu amfani da iskar gas (CNG) don sauƙaƙa rabon mai ba tare da cajin ƙarin kuɗin sufuri ba.

Za su raba mai kai tsaye ga masu gidajen mai da masana’antu da kamfanonin sadarwa da sauran manyan masu amfani da mai.

Kamfanin ya kuma sanar da bada bashin sati biyu ga waɗanda ke sayen lita 500,000 na fetur ko man gas na dizil, inda za a ba su ƙarin lita 500,000 a bashi idan sun cimma sharaɗi (banki).

Dangote ya ce wannan mataki ya yi daidai da manufar tattalin arzikin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu.

Sai dai wasu ƙungiyoyin kamar PETROAN da MEMAN sun nuna damuwa, suna cewa wannan tsarin zai iya haifar da ƙarancin aiki a sashen rarraba mai da kuma haɗarin kankane aikin raba man ga kamfani ɗaya

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp