Kamfanin Dangote ya kaddamar da wani shiri na musamman na horas da ‘yan jarida sittin a Kano, a wani bangare na ayyukanta na zamantakewar al’umma.
A cewar kamfanin, horon an yi shi ne da nufin kara kaimi kan fasahar sadarwa, wanda aka zabo daga jihohin Arewa maso Yamma ciki akwai Sokoto, Katsina, Kebbi, Kano, Kaduna, Zamfara da kuma Jigawa.
Solacebase ta rawaito cewa, horon haɗin gwiwa ne tare da Folio Media and Creative Academy kuma an gudanar da shi a baya a wasu shiyyoyin ƙasar nan.
Taron na kwanaki uku mai taken: “The Convergence Journalism”.
A taron wanda aka fara gudanar da shi jihar a Kano ranar Laraba, wanda babban Jami’in Kamfanin, Branding and Communication, Anthony Chiejina, ya ce an shirya horaswar ne, domin inganta kwazon ‘yan jarida kan dabarun yada labarai.
Ya ce” horon zai taimaka wajen samar wa manema labarai damar tunkarar kalubalen da ke tattare da su musamman ma, sabbin kafafen yada labarai tare da bayyana kafafen yada labarai a matsayin abokan hadin gwiwa da ake samu. Inji Anthony.
Mai gudanar da yyyukan na Folio Media and Creative Academy, Alabi Pius, ya ce, “(FMCA) ita ce ta horar da Folio Communications Plc. Mawallafin jaridar Daily Times, kuma wannan horon zai baiwa ‘yan jarida da shugabannin kafafen yada labarai da jami’an hulda da jama’a da sauran kwararru a aikin”.