fidelitybank

Dan takarar Gwamna da ‘yan takarar majalisa a Jigawa sun koma APC daga LP

Date:

‘Yan takarar gwamna na jam’iyyar Labour a jihar Jigawa, Tsoho Garba da dukkan ‘yan takarar majalisar wakilai ta kasa sun sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.

Tsoho Garba ya tabbatar da haka a ranar Asabar bayan ganawa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Dutse babban birnin jihar.

Sai dai ya ce, shugaban jam’iyyar LP na jihar da kusan dukkanin shugabannin jam’iyyar na kananan hukumomi 27 na jihar sun koma jam’iyyar APC.

Tsoho ya ce sun yanke shawarar janye takararsu da jam’iyyarsu ta APC ne domin nuna godiya ga gagarumin ci gaban da Gwamna Badaru Abubakar ya yi a jihar.

“Mutane sun bukaci mu tsaya takara a karkashin jam’iyyar Labour, amma a ziyarar yakin neman zaben da muka yi a fadin jihar duk mun san yadda gwamnatin APC ta sauya jihar ta hanyar ayyuka da shirye-shirye masu tasiri kai tsaye ga talaka”.

“Idan har muna takara ne domin neman ci gaban jiharmu, babu shakka abin da Jigawa ke bukata shi ne a ci gaba da zama, kuma abin da ya fi dacewa shi ne a bar APC ta ci gaba da jan ragamar mulki domin kada ta kauce daga babbar hanyar. ”

“Don haka daga yau dukkanmu da abokan siyasarmu mun koma APC kuma mun sha alwashin yin aiki domin samun nasarar ta a matakin kasa da jiha a babban zabe mai zuwa”.

Da yake karbar wadanda suka sauya sheka, Gwamna Badaru Abubakar ya yaba da kudurinsu na ci gaban jihar tare da yi musu alkawarin ba su duk wani hakki da tsofaffin ‘ya’yan jam’iyyar suka samu.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp