fidelitybank

Dan takarar Gwamna da ‘yan takarar majalisa a Jigawa sun koma APC daga LP

Date:

‘Yan takarar gwamna na jam’iyyar Labour a jihar Jigawa, Tsoho Garba da dukkan ‘yan takarar majalisar wakilai ta kasa sun sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.

Tsoho Garba ya tabbatar da haka a ranar Asabar bayan ganawa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Dutse babban birnin jihar.

Sai dai ya ce, shugaban jam’iyyar LP na jihar da kusan dukkanin shugabannin jam’iyyar na kananan hukumomi 27 na jihar sun koma jam’iyyar APC.

Tsoho ya ce sun yanke shawarar janye takararsu da jam’iyyarsu ta APC ne domin nuna godiya ga gagarumin ci gaban da Gwamna Badaru Abubakar ya yi a jihar.

“Mutane sun bukaci mu tsaya takara a karkashin jam’iyyar Labour, amma a ziyarar yakin neman zaben da muka yi a fadin jihar duk mun san yadda gwamnatin APC ta sauya jihar ta hanyar ayyuka da shirye-shirye masu tasiri kai tsaye ga talaka”.

“Idan har muna takara ne domin neman ci gaban jiharmu, babu shakka abin da Jigawa ke bukata shi ne a ci gaba da zama, kuma abin da ya fi dacewa shi ne a bar APC ta ci gaba da jan ragamar mulki domin kada ta kauce daga babbar hanyar. ”

“Don haka daga yau dukkanmu da abokan siyasarmu mun koma APC kuma mun sha alwashin yin aiki domin samun nasarar ta a matakin kasa da jiha a babban zabe mai zuwa”.

Da yake karbar wadanda suka sauya sheka, Gwamna Badaru Abubakar ya yaba da kudurinsu na ci gaban jihar tare da yi musu alkawarin ba su duk wani hakki da tsofaffin ‘ya’yan jam’iyyar suka samu.

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp