fidelitybank

Dalilin mayar da dukannin karar shari’ar gwamna zuwa Abuja – Mai Shari’a Monica

Date:

Shugabar Kotun Daukaka Kara a Najeriya, Mai Shari’a Monica Dongban-Mensem, ta ba da umarnin a mayar da duk kararrakin da aka daukaka na shari’o’in zaben watan Fabrairu da na Maris zuwa Abuja da Legas.

Tashar talbijin ta Channels TV ta ruwaito cewa umarnin ya shafi dukkan kararrakin da aka daukaka na zaben gwamnoni, da na ‘yan majalisar tarayya, da kuma na jihohi.

Tashar ta ce kararrakin da aka daukaka daga kotunan sauraron zabe a jihohi, kamata ya yi a saurare su a kotunan daukaka kara 20 da ke fadin kasar, amma yanzu rassan kotun biyu ne kacal za su yi alkalanci a kansu.

Channels ta ambato majiyoyi a Kotun Daukaka Karar na cewa reshen kotun na Abuja ne zai saurari kararrakin zaben da aka daukaka daga jihohi 19, yayin da kararrakin zabe na jihohin kudu 17 za a saurare su a Legas.

Ta ce an ba da umarnin ne bayan zarge-zarge da korafe-korafen da aka shigar a kan alkalan kotunan jihohi.

Wasu jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu sun yi zargin cewa wasu sun sanya alkalan kotunan zabe karya ka’idar aiki.

Ta ce jam’iyyun da suka fusata sun kuma nuna damuwar cewa irin haka ce mai yiwuwa za ta faru idan aka saurari kararrakin da aka daukaka a jihohi.

Mai Shari’a Monica Dongban-Mensem kamar yadda Channels ta ruwaito, na cewa mayar da shari’o’i zuwa sassan kotun kalilan zai ba ta damar sanya ido a kan alkalan yadda ya kamata.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp