fidelitybank

Dalilin da ya sa ICPC ta sake ni – Mawaki D’Banj

Date:

Mawaki, Oladapo Oyebanji, Dbanj ya bayyana dalilin da ya sa hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta (ICPC) ta sake shi daga tsarewar da ta yi masa.

Ku tuna cewa an tsare Dbanj ranar Laraba bisa zargin hada baki da wasu ‘yan siyasa da bankuna domin karkatar da kudaden N-power.

Mawakin dai ta bakin lauyansa ya ce ba shi da wata alaka ta kwangila ko wata alaka da wata kungiya ko mutane a ciki ko wajen Gwamnati.

Ya kuma kalubalanci ICPC da ta bayyana sunayen jami’ai da ‘yan siyasa, wadanda ke da hannu a cikin yarjejeniyar.

Sai dai an sake Dbanj a ranar Juma’a, bayan shafe kwanaki uku a tsare.

Da yake rubutawa a shafinsa na Instagram, Dbanj ya ce, an sake shi ne bisa son ransa saboda ICPC ba ta samu komai a kansa ba.

Ya kuma godewa ‘yan Najeriya tare da bayyana kwarin gwiwar cewa ICPC za ta bankado gaskiya.

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp