fidelitybank

Dalilin da ya sa a ka aiyana ƴan fashin daji a matsayin ƴan ta’adda — Osinbajo

Date:

 

 

 

 

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Farfesa Yemi Osinbajo, ya ce dalilin da ya sa gwamnatin tarayya ta aiyana ‘yan fashin daji a matsayin ƴan ta’adda a hukumance shi ne don baiwa jami’an tsaro damar ɗaukar tsauraran matakai a kansu.

Mataimakin shugaban ƙasan ya baiyana haka ne a fadar Sarkin Katsina a ranar Asabar domin yin ta’aziyya ga Dahiru Barau Mangal, wanda ya rasa mahaifiyarsa, Hajiya Murja.

Osinbajo ya kuma baiyana fatansa na cewa dukkan sabbin matakan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarta sun sanya ya kamata a iya ganin sauyi mai ma’ana sosai a harkar tsaron Nijeriya.

Yayin da yake mika godiyarsa ga Sarkin Katsina da sarakunan sa bisa kyakkyawar tarba da aka yi masa, Osinbajo ya yi addu’ar Allah ya ba wa masarautarsa ​​da ƙasa baki daya zaman lafiya.

Ya baiyana ƙwarin gwiwa ce za a samu wadata da farin ciki da kuma zaman lafiya a ƙasar nan kafin wa’adin mulkinsu ya ƙare.

Da yake mayar da martani, Sarkin Katsina, ya bayyana farin cikinsa da ayyana ‘yan bindiga a matsayin ‘yan ta’adda a hukumance.

 

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp