fidelitybank

Daliban Kano 3 sun shiga jerin sahun wadanda a ka fi kafa hujja da su a fanin kimiyya na duniya

Date:

Wasu dalibai 3 da toshon gwamnatin, Dr. Rabi’u Musa Kwankwaso ta dauki nauyin karatun su, Drs Aliyu Isa Aliyu da Tukur Abdulkadir Sulaiman, da kuma Abdullahi Yusuf, sun shiga cikin jerin sahun gaba na cikin kashi 2 na masana kimiyya wadan da a ka fi nema a duniya.

Jerin sunayen su, wanda a ka buga a watan Agusta 2021, a cikin ƙungiyar masu bincike ne suka shirya wanda, Farfesa John Loannidis na Jami’ar Stanford, California da ke Amurka.

Jerin ya haɗa da masu bincike sama da 100,000 waɗanda a ka zaɓa tsakanin masana kimiyya sama da miliyan 8 a cikin fagagen kimiyya 22 da ƙananan 176 a duk faɗin duniya.

Daily Nigerian ta rawaito cewa, an haifi Dr. Abdullahi Yusuf a karamar hukumar Dala a jihar Kano. Ya kammala karatunsa a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Kano a shekarar 2010. Ya samu digirin digirgir (Ph.D) a Applied Mathematics daga jami’ar Firat University, Elazig ta kasar Turkiyya a 2019.

An haifi Dr. Tukur Abdulkadir Sulaiman a karamar hukumar Kiru da ke jihar Kano. Ya kammala karatunsa a Jami’ar Bayero Kano a shekarar 2009. Ya samu digirin digirgir (Ph.D). wanda ya yi karatu a fannin lisafi na Applied Mathematics a jami’ar Firat, Elazig, Turkiyy a 2019.

An haifi Dr. Aliyu Isa Aliyu a karamar hukumar Bichi ta jihar Kano. Ya kammala karatunsa a Jami’ar Bayero Kano a shekarar 2009. Ya samu digirin digirgir (Ph.D) na Applied Mathematics a jami’ar Firat Elazig, Turkiyya a 2018.

Matasan malaman uku na daga cikin wadanda su ka ci gajiyar tallafin karatu na kasashen waje na gwamnatin jihar Kano a zamanin Gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso daga 2011 zuwa 2014. An dauki nauyin karatunsu a shekarar 2012 domin yin digiri na biyu a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Jordan da ke Irbid ta kasar Jordan.

Mutanen uku a halin yanzu su na aiki da Sashen Lissafi na Jami’ar Tarayya Dutse da ke Jigawa a Najeriya.

 

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp