fidelitybank

Daliban Kano 3 sun shiga jerin sahun wadanda a ka fi kafa hujja da su a fanin kimiyya na duniya

Date:

Wasu dalibai 3 da toshon gwamnatin, Dr. Rabi’u Musa Kwankwaso ta dauki nauyin karatun su, Drs Aliyu Isa Aliyu da Tukur Abdulkadir Sulaiman, da kuma Abdullahi Yusuf, sun shiga cikin jerin sahun gaba na cikin kashi 2 na masana kimiyya wadan da a ka fi nema a duniya.

Jerin sunayen su, wanda a ka buga a watan Agusta 2021, a cikin ƙungiyar masu bincike ne suka shirya wanda, Farfesa John Loannidis na Jami’ar Stanford, California da ke Amurka.

Jerin ya haɗa da masu bincike sama da 100,000 waɗanda a ka zaɓa tsakanin masana kimiyya sama da miliyan 8 a cikin fagagen kimiyya 22 da ƙananan 176 a duk faɗin duniya.

Daily Nigerian ta rawaito cewa, an haifi Dr. Abdullahi Yusuf a karamar hukumar Dala a jihar Kano. Ya kammala karatunsa a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Kano a shekarar 2010. Ya samu digirin digirgir (Ph.D) a Applied Mathematics daga jami’ar Firat University, Elazig ta kasar Turkiyya a 2019.

An haifi Dr. Tukur Abdulkadir Sulaiman a karamar hukumar Kiru da ke jihar Kano. Ya kammala karatunsa a Jami’ar Bayero Kano a shekarar 2009. Ya samu digirin digirgir (Ph.D). wanda ya yi karatu a fannin lisafi na Applied Mathematics a jami’ar Firat, Elazig, Turkiyy a 2019.

An haifi Dr. Aliyu Isa Aliyu a karamar hukumar Bichi ta jihar Kano. Ya kammala karatunsa a Jami’ar Bayero Kano a shekarar 2009. Ya samu digirin digirgir (Ph.D) na Applied Mathematics a jami’ar Firat Elazig, Turkiyya a 2018.

Matasan malaman uku na daga cikin wadanda su ka ci gajiyar tallafin karatu na kasashen waje na gwamnatin jihar Kano a zamanin Gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso daga 2011 zuwa 2014. An dauki nauyin karatunsu a shekarar 2012 domin yin digiri na biyu a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Jordan da ke Irbid ta kasar Jordan.

Mutanen uku a halin yanzu su na aiki da Sashen Lissafi na Jami’ar Tarayya Dutse da ke Jigawa a Najeriya.

 

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp