fidelitybank

Daga yanzu babu wanda zai sake raina mai zaɓe a Najeriya – Buhari

Date:

Shugaba Muhammadu Buhari, ya ce, zaɓukan 2023 sun nuna yadda mulkin dimokuraɗiyya ke ci gaba da ginuwa da kuma samun karfi musamman ma ta yadda masu zaɓe suka waye da kuma sanin shugabannin da za su zaɓa.

Shugaba Buhari ya bayyana haka ne lokacin da ya karɓi bakuncin sabon Sarkin Dutse, Alhaji Muhammad Hamim Nuhu a fadarsa da ke Abuja, inda ya ce, sakamakon zaɓen gwamnoni guda 10 da suka kasa samun nasarar zuwa majalisar dattawa, ya nuna cewa yanzu babu tabbas game da samun mulki kuma yanzu masu zaɓe su ke da wuƙa da nama.

Karanta Wannan: Ɗan takarar mu Obi ake hari ba jam’iyyar mu ba – LP

“Hakan ya nuna cewa, dimokuraɗiyyar mu na ƙara girma da kuma yadda masu zaɓe suka waye. Abin da ya bani mamaki shi ne ɗan Najeriyar da aka raina, a yanzu shi ke da wuƙa da nama wajen zaɓar wanda ya dace,” in ji Buhari.

“An mayar da cewa bayan gwamna ya yi shekara takwas, daga nan zai tafi majalisar dattawa ba tare da shan wahala ba. Daga yanzu babu wanda zai sake raina mai zaɓe a Najeriya. Siyasa za ta zama abu mafi wahala nan gaba,” a cewar Buhari.

Da yake magana, sabon Sarkin na Dutse, Alhaji Muhamamd Hamim, ya gode wa gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari saboda taimaka wa jihar Jigawa ta samu ci gaba a ɓangaren noman shinkafa da amincewa da gina layin dogo daga Kano zuwa Dutse da kuma dawo da zaman lafiya a jihar

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp