Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane da hare-haren da Isra’ila ta kai kan Iran kafin ta kai amma ya jaddada cewa babu hannun Amurka a ciki.
Trump ya bayyana hakan ne a tattaunawarsa da Fox news dangane da hare-haren.
Ya kuma maimaita cewa yana fatan Iran za ta ci gaba da tattaunawa da Amurka domin rage barazanar shirinta na makaman nukiliya.
“Iran ba za ta mallaki bam na nukiliya ba, kuma muna fatan komawa teburin tattaunawa.” in ji shi a hirarsa da tashar talabijin na Fox News.
Ya ƙara da cewa, “Akwai wasu daga cikin shugabannin Iran da ba za su sake dawowa ba,” yana nuni da cewa Amurka ta tabbatar da mutuwar wasu shugabannin Iran a harin.
Trump ya ce gwamnatinsa ta tuntubi wata muhimmiyar ƙasa kawarta a Gabas ta Tsakiya kafin a kai harin don sanar da su, sai dai bai ambaci sunan kasar ba.