fidelitybank

Da Dumi-Dumi: ‘Yan bindiga sun yi awon gaba da mutane a kauyen Zamfara

Date:

Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne, sun yi garkuwa da wasu mutanen kauyen Zurmi da ke karamar hukumar Zurmi a jihar Zamfara da ba a tantance adadinsu ba.

THEWILL ta ruwaito cewa, ‘yan bindigar sun mamaye kauyen ne a ranar Alhamis inda suka yi garkuwa da mutanen kauyen da dama.

Wani mazaunin unguwar da ya nemi a sakaya sunansa ya ce ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyen ne da misalin karfe 10 na dare, inda suka fara harbe-harbe a sama.

Ya lura cewa ‘yan bindigar ba su kashe kowa ba, saboda a fili suna so su sace mutanen kauyen.

“Duk da cewa ba su kashe kowa ba, sun yi awon gaba da wasu mutanen da ba a tantance adadinsu ba a yayin aikin. Kwanaki uku da suka wuce, sun kashe mutum daya tare da satar shanu,” inji shi.

Har yanzu dai rundunar ‘yan sandan jihar ba ta mayar da martani kan lamarin ba, har ya zuwa lokacin hada wannan rahoto.

A wani labarin kuma, rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta sanar da kama wasu mutane shida da ake zargi da hannu a rikicin kananan hukumomin Guyuk da Lamurde da ya yi sanadiyar mutuwar wasu mutane.

Rundunar a kokarinta na ganin ta kawo karshen rikicin da ya barke a unguwannin kananan hukumomin, ta kama mutane kusan shida da ake zargi da hannu a rikicin.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...
X whatsapp