Matuka Babura mai kafa uku a jihar Kano, za su koma bakin aikin su a gobe Alhamis, sakamaon zaman sulhu da su ka yi da gwamnatin Kano.
Lauyan masu Baburan, Barista Abba Hikima Fagge ne ya tabbatar da hakan yayin ganawa da manema labarai a yammacin ranar Talata.
Yayin zaman an cimma matsaya kamar haka:
1. Za a rubutawa gwamnatin jihar kano takardar Neman ragin kudin sabunta rigistar na naira dubu 8.
2. Yan adaidaita Sahu za su dawo aiki a gobe alhamis.
3 . Za a jira gwamnatin ta tsaida matsaya kafin ranar 18 ga wannnan watan da za a sake zama.
4 . Yan Adaidaita Sahu za su cigaba da biyan Naira 100 harajin kullum-kullum.
Wadannan dai su ne abun da a ka cimma yayin zaman da a ka gudanar a yau a ofishin Kungiyar lauyoyi ta kasa reshen jihar Kano, kuma yayin zaman kowanne bangare ya aminta da duk abubuwan da a ka gindaya.