fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Buhari ya umarci sojoji su murkushe ‘yan ta’adda Neja

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bukaci sojoji da su mayar da martani mai karfin gaske kan lamarin kashe-kashe da garkuwa da mutane a jihar Neja tare da tabbatar da dabarun da aka sa a gaba ta hanyar amfani da karfi.

Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai, Garba Shehu ne ya tabbatar da hakan a ranar Lahadi, ya ce, shugaban ya bayar da umarnin ne ga shelkwatar tsaro.

Ya ce”shugaba Buhari a matsayinsa na babban kwamandan sojojin kasar nan ya shirya wani gagarumin farmakin soji a jihar Neja wanda ya ci gaba da fuskantar hare-haren ‘yan bindiga da ragowar ‘yan ta’addan Boko Haram a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabashin kasar nan”.

A sakonsa ga gwamnati da al’ummar jihar Neja, shugaba Buhari ya ce, “Ina so in mika sakon ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar jihar, sakamakon matsalolin tsaro da suka faru a baya-bayan nan. Tsaro hakki ne na kowane memba na al’umma kuma ta hanyar hadin kai da hadin gwiwa da hukumomin tabbatar da doka, zamu iya shawo kan matsalolin a karshe”.

“Gwamnatin tarayya a shirye take ta karfafa goyon baya da hadin gwiwa da dukkan jihohin. Na yi imanin cewa tare da cikakken hadin kan ‘yan kasa, tabbas za mu shawo kan wannan matsala,” in ji shugaban kasar a cikin sanarwar mai taken “Big military Operation in Niger”.

A ranar Talatar da ta gabata ne ‘yan ta’adda suka mamaye al’umomin karamar hukumar Shiroro ta Neja, inda suka kashe mutane akalla 13 a wani harin da suka kai da rana a Nakundna da Wurukuchi.

Harin na ranar Talata ya zo ne kasa da makwanni biyu bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari kan ma’aikata a madatsar ruwan Zungeru, inda suka kashe mutane biyu tare da yin garkuwa da wasu ‘yan kasar China uku.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp