fidelitybank

DA ƊUMI-ƊUMI: Ƴan ta’adda sun sako mutane 60 da su ka ɗauke a coci a Kaduna

Date:

 

Bayan wata ɗaya a hannun masu garkuwa da mutane, masu bauta a cocin emanuel baftis da ke Kakau Daji, Jihar Kaduna sun shaƙi iskar ƴanci.
A ranar 31 ga watan Oktoba ne dai masu ibadar su na tsaka da bauta a cikin cocin, sai ƴan yadda su ka dirar musu, inda su ka yi awon-gaba da mutum 60 da ga cikin su.
Bayan ƴan kwanaki, sai ƴan ta’addan su ka hallaka uku da ga ciki sannan su ka kaiwa biyu munanan raunuka bayan sun nemi a basu kuɗin fansa.
Shugaban Ƙungiyar Kiristoci ta Ƙasar, reshen Jihar Kaduna, Rabaran Joseph John Hayab ne ya baiyana sakin masu bautar a yau Asabar.
Ya ƙara da cewa a kwai wasu mutane 9 ma da a ka sake su tare da ƴan cocin a jiya Juma’a da daddare.
Sai dai kuma Hayab bai baiyana cewa ko sai da a ka biya kuɗin fansa sannan a ka saki masu bautar ba, ya ce dai kawai ma’aikatan cocin ne su ka sanar da shi sannan sojoji sun tafi da su bariki.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp