A yayin da yake kaddamar da sabon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, Salisu Yusuf (D–Black), Gwamnan jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje ya umarce shi da ya nuna kwarewarsa domin kai kungiyar ga tudun mun tsira.
Ya ce Salisu D-Black ya kasance mai horar da ‘yan wasan Super Eagles ta kasa, su na da kwarin gwiwa da shi a kan jagorancin al’amura na wasanni, zai kuma mayar da Kano Pillars zuwa matsayin da ya dace a gasar cin kofin Nahiyar Afrika.
Da yake jawabi kwamishinan matasa da wasanni, Kabiru Ado Lakwaya ya bayyana shirin a matsayin ci gaba da gwamnatin Ganduje ta bullo da shi, domin bunkasa harkokin wasanni.