Shugaba Muhammadu Buhari ya yi watsi da wasu karin ayyuka 6,576 da Majalisar Dokokin ta ƙara a kasafin kudin 2022.
Buhari wanda ya bayyana hakan yayin sanya wa kasafin hannu a fadarsa da ke Abuja, ya ce, zai sa ke mayar wa ƴan majalisar, domin su duba gyare-gyaren da ya yi.
Shugaban ya ce, sanya ayyukan da kuɗin ya haura Naira biliyan 36 ya saɓa wa dokar cin gashin kai da kowanne ɓangaren zartarwa ke da shi.
Sai dai shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan ya kafe a kan cewa, babu kuskure a abun da su ka yi, yan a cewa, dama ba lallai ne a ce a ko da yaushe ra’ayin ɓangarorin biyu ya zo ɗaya ba. A cewar BBC.