Ministan harkokin cikin gida a Najeriya, Rauf Aregbesola, ya ce kashi 74 na mazauna gidan ajiya da gyaran hali na jiran shari’a ne.
Ministan na magana ne yayin ƙaddamar da shirin aiwatar da shari’o’i ta intanet karon farko a Najeriya ta hanyar taimako daga hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta UNDP da kuma gwamnatin ƙasar Japan.
Rauf Aregbesola wanda ma’aikatarsa ce ke kula da gidajen yarin ƙasar ya ce, adadin mai yawa na samuwa ne sakamakon ƙaruwar ɓalla gidajen ajiya da gyaran hali da ake yi a baya-bayan nan.
A cewarsa,”Fursuna 17,000 ne kaɗai daga cikin 68,000 aka yanke wa hukunci yayin da sauran ke jiran shari’a. Hakan na alaƙa ne da tafiyar hawainiya da ake samu a tsarin shari’ar Najeriya, da yawa daga cikin ɗaurarrun kan mutu kafin a yanke musu hukunci,”. inji Rauf.
A ‘yan kwanakin nan, ƙungiyoyin ‘yan bindiga a Najeriya kan kai wa gidajen yari hare-hare da zummar kuɓutar da mambobinsu. Inji BBC.