Mai martaba sarkin Adamawa, Lamidon Adamawa, Muhammadu Barkindo, ya tsige guda daga cikin mai rike da sarautar gargajiya a jihar, bisa sukar, Gwamna jihar Ahmadu Fintiri kan bayar da kyautar mota ga sarakunan gargajiya a jihar.
Majalisar Masarautar Adamawa ta ce yanzu Umar Mustapha bai cancanci rike sarautar gargajiya ta ‘Mukaddas Adamawa’ ba. Sakamakon sukar da ya yi.
Mustapha wanda tsohon dan takarar gwamna ne a karkashin jam’iyyar APC, a wata sanarwa da ya fitar ya caccaki gwamna Ahmadu Fintiri kan kyaututtukan da ya yi.
“Abin da bai dace ba ne a kashe Naira miliyan 200 domin samun motoci ga sarakunan gargajiya yayin da ‘yan fansho ke mutuwa saboda yunwa,” inji Tsohon Mukaddas Adamawa Umar.
Sanarwar ta biyo bayan sanarwar da gwamnatin jihar ta yi wa sarakunan gargajiya.
Bayan sanarwar, Sarkin, Barkindo, a wata sanarwa ta hannun sakataren masarautar, Khalil Kawu, ya ce an tsige Mustapha daga mukamin sa.