Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yi fatan ‘yan wasan Najeriya da ke halartar gasar Olympics da na nakasassu a birnin Beijing na shekarar 2022 da su yi kokari wajen ganin sun samu nasara a gasar.
Shugaba Buhari ya yi imanin cewa ‘yan wasan Najeriya da ke halartar gasar daban-daban za su yi fice a gasar, inda za su wuce tarihin da aka taba yi a PyeongChang na Koriya ta Kudu a shekarar 2018, lokacin da al’ummar kasar suka fafata a karon farko.
Ganin cewa gasar Olympics wani dandali ne na sada zumunta da hadin gwiwa tsakanin kasashe, shugaba Buhari ya na fatan dukkan ‘yan wasa a kokarin cimma burinsu na Olympics, za su inganta muhimman dabi’un wasannin.
Shugaban kasar Sin ya taya kasar Sin murnar karbar bakwancin gasar Olympics ta lokacin sanyi, ya na mai yabawa birnin Beijing bisa kafa tarihi a matsayin “birni na Olympics” na farko a tarihin Olympics, bayan da ya karbi bakuncin gasar Olympics ta lokacin zafi a shekarar 2008.