Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yi Allah wadai da harin da aka kaiwa ‘yan banga a dajin Yargoje da ke karamar hukumar Jibia a jihar Katsina, inda aka yi asarar rayuka da dama.
‘Yan ta’addan sun yi wa ayarin ‘yan banga kwanton bauna a cikin dajin a lokacin da suka je kwato shanun da suka sato da ya kai ga kashe su.
Karanta Wannan: ;Yan bindiga sun kashe mutane 41 a Katsina
A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Garba Shehu ya sanyawa hannu.
“Shugaban ya jinjinawa duk ‘yan banga da ‘yan uwa da suka yi shahada a yau, yana mai cewa ba za a manta da sadaukarwar da jajirtattun maza da ke aiki don dakile aikata laifuka a cikin al’ummarsu ba.”
Shehu ya ruwaito shugaban yana mai cewa, “Tunaninmu da addu’o’inmu suna tare da iyalan wadanda suka rasa rayukansu a wannan mawuyacin lokaci. Allah ya jikan mamacin”.