A ranar Laraba ne shugaban kasa Muhammadu Buhari zai tashi daga Abuja zuwa Banjul na kasar Gambia, domin halartar bikin rantsar da shugaban kasar Gambia, Adama Barrow, bayan sake zabensa a karo na biyu.
Garba Shehu, mai taimaka wa shugaban kasa kan harkokin yada labarai ne ya tabbatar da hakan, a wata sanarwa a ranar Talata a Abuja.
Kamfanin dillancin labarai na kasa NAN yarawaito cewa, Shehu ya ce: “A bisa gayyatar mai masaukin nasa, shugaba Buhari zai kasance babban bako na musamman a wajen bukukuwan da sauran shugabannin Afirka za su halarta a filin wasa na Independence, Bakau.”
Buhari, tare da wasu shugabannin kungiyar ECOWAS, sun taka rawa wajen mayar da mulkin dimokuradiyya a Gambia a shekarar 2017, bayan da tsohon shugaban kasar Yahya Jammeh ya ki mika mulki bayan ya sha kaye a zabe.
Shugaban zai samu rakiyar Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno da Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa, Amb. Ahmed Rufa’i, da sauran manyan jami’an gwamnati.
Ana sa ran shugaban zai dawo Najeriya a karshen bikin rantsar da shi.