fidelitybank

Buhari ya tafi Gambia rantsar da shugaban kasa

Date:

A ranar Laraba ne shugaban kasa Muhammadu Buhari zai tashi daga Abuja zuwa Banjul na kasar Gambia, domin halartar bikin rantsar da shugaban kasar Gambia, Adama Barrow, bayan sake zabensa a karo na biyu.

Garba Shehu, mai taimaka wa shugaban kasa kan harkokin yada labarai ne ya tabbatar da hakan, a wata sanarwa a ranar Talata a Abuja.

Kamfanin dillancin labarai na kasa NAN yarawaito cewa, Shehu ya ce: “A bisa gayyatar mai masaukin nasa, shugaba Buhari zai kasance babban bako na musamman a wajen bukukuwan da sauran shugabannin Afirka za su halarta a filin wasa na Independence, Bakau.”

Buhari, tare da wasu shugabannin kungiyar ECOWAS, sun taka rawa wajen mayar da mulkin dimokuradiyya a Gambia a shekarar 2017, bayan da tsohon shugaban kasar Yahya Jammeh ya ki mika mulki bayan ya sha kaye a zabe.

Shugaban zai samu rakiyar Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno da Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa, Amb. Ahmed Rufa’i, da sauran manyan jami’an gwamnati.

Ana sa ran shugaban zai dawo Najeriya a karshen bikin rantsar da shi.

 

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Æ´an Æ™asarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan ÆŠaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp