fidelitybank

Buhari ya tafi Gambia rantsar da shugaban kasa

Date:

A ranar Laraba ne shugaban kasa Muhammadu Buhari zai tashi daga Abuja zuwa Banjul na kasar Gambia, domin halartar bikin rantsar da shugaban kasar Gambia, Adama Barrow, bayan sake zabensa a karo na biyu.

Garba Shehu, mai taimaka wa shugaban kasa kan harkokin yada labarai ne ya tabbatar da hakan, a wata sanarwa a ranar Talata a Abuja.

Kamfanin dillancin labarai na kasa NAN yarawaito cewa, Shehu ya ce: “A bisa gayyatar mai masaukin nasa, shugaba Buhari zai kasance babban bako na musamman a wajen bukukuwan da sauran shugabannin Afirka za su halarta a filin wasa na Independence, Bakau.”

Buhari, tare da wasu shugabannin kungiyar ECOWAS, sun taka rawa wajen mayar da mulkin dimokuradiyya a Gambia a shekarar 2017, bayan da tsohon shugaban kasar Yahya Jammeh ya ki mika mulki bayan ya sha kaye a zabe.

Shugaban zai samu rakiyar Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno da Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa, Amb. Ahmed Rufa’i, da sauran manyan jami’an gwamnati.

Ana sa ran shugaban zai dawo Najeriya a karshen bikin rantsar da shi.

 

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuÉ—in gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuÉ—in gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuÉ—a

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiÉ—a wa Isra'ila wasu...
X whatsapp