Gwamnan jihar Bineu, Samuel Ortom, ya yi kira ga shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari da ya ayyana wasu ƙungiyoyin Fulani makiyaya kamar su Miyetti Allah Kautal Hore da Kungiyar Mi Yetti Allah (wato MACBAN), da kuma Fulani Nationality Movement (wato FUNAM) a matsayin ‘yan ta’adda su ma.
A cewar Gwamna Ortom, ayyana ‘yan fashin daji a matsayin ‘yan ta’adda kaɗai da gwamnatin Najeriya ta yi bai isa ba hakan nan.
Ya dai zargi ƙungiyoyin Fulanin da lasar takobi da kuma ci gaba da haddasa gagarumin yamutsi a jihar Binuwai da ma sauran yankunan ƙasar saboda dokokin hana kiwon.
Ɗaya daga cikin kungiyoyin da gwamnan ya ambata dai ta yi watsi da wannan kira, wanda suka bayyana da cewa, wani bi ta da kulli ne kawai.