Shugaban kasa Muhammadu Buhari na wata ganawa ta musamman da jagoran jam’iyar APC, Bola Tinubu.
Tattaunawar na zuwa ne a fadar Villa a tsakanin shugaba Buhari da Tinubu jigon jam’iyyar APC.
Sai dai har yanzu jagororin biyu na ci gaba da ganawa a tsakanin juna, kawo wannan lokaci, wanda dazarar sun kammala za mu ci gaba da sanar da ku halin da a ke ciki a tsakanin Buhari da Tinubu.
Tattaunawar ba za ta wuce nasabar karatowar zaben shugaban kasa a shekarar 2023, wanda wasu daga cikin kungiyoyi ke zawarcin Tinubu ya fito takarar shugaban kasa a shekarar 2023.
Jiga-jigan ‘yan siyasa da dama na zawarcin kujerar shugaban kasa a zaben 2023,