fidelitybank

Bugun Zuciya: Kanin Maradona Hugo ya mutu

Date:

Hugo Maradona wanda kanin fitaccen dan wasan kwallon kafa na Argentina, Diego, ya mutu sakamakon bugun zuciya.

Hugo mai shekaru 52 ya fuskanci bugun zuciyar ne a gidansa da ke Naples. Hugo ya mutu da misalin karfe 11.50 na safiyar Talata.

Hakan na zuwa ne watanni 13 kacal bayan da bugun zuciya ya kashe Diego Maradon, gwarzon gasar cin kofin duniya na Argentina kuma daya daga cikin mafi girma da ya taba buga wasan wanda ya mutu a Argentina a watan Nuwamba 2020 ya na da shekaru 60.

Kafin rasuwar Hugo an hango shi filin wasa na Maradona da ke Naples ta kasar Italiya, domin halartar bikin tunawa da dan uwansa marigayi kuma fitaccen dan wasan kwallon kafa wata daya kacal da ya wuce.

Kafin rasuwar sa ya dai bar mace mai suna Paola Morra, wadda ya aura a shekara ta 2016, tare da ’ya’ya uku.

Ƙananan ‘yan’uwan Maradona da sauran su ne Diego da Raul da Hugo shi ma dan wasan Æ™wallon Æ™afa ne kuma ya sanya hannu tun ya na matsayin matashi ga kungiyar Napoli mai shekaru 18 a 1987.

Amma ba kamar É—an’uwansa ba, wanda ya buga wasa mafi kyawun shekarunsa a Napoli kuma a na girmama shi a birnin Naples ta kasar Italiya a matsayin wani mutum mai daraja.
A ranar 20 ga Satumba, 1987, ‘yan’uwan biyu sun yi wasa da juna tare da Napoli wanda a ka buga 2-1.

Hugo, wanda ya kasance tauraron tawagar Argentina a gasar cin kofin matasa na duniya na FIFA na matasa ‘yan kasa da shekaru 16 a shekarar 1985, wanda ya kasance kan gaba a gasar cin kofin duniya na ‘yan kasa da shekaru 17, ya ci gaba da taka leda a kananun gasa na Spain da Austria da Venezuela kafin ya kawo karshen aikinsa na buga wasa a Japan a karshen shekarun 1990.

Bayan haka ya koma horarwa, kuma ya shiga cikin ajin manyan makarantun matasa a matsayin masu horaswa.

vanguard 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci Æ™arya ne – Ƴansanda

Rundunar Æ´ansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaÉ—awa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...

Mayakan IS sun yi wa Sojojin Najeriya barna a kwana biyu

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari,...
X whatsapp