fidelitybank

Bugun Zuciya: Kanin Maradona Hugo ya mutu

Date:

Hugo Maradona wanda kanin fitaccen dan wasan kwallon kafa na Argentina, Diego, ya mutu sakamakon bugun zuciya.

Hugo mai shekaru 52 ya fuskanci bugun zuciyar ne a gidansa da ke Naples. Hugo ya mutu da misalin karfe 11.50 na safiyar Talata.

Hakan na zuwa ne watanni 13 kacal bayan da bugun zuciya ya kashe Diego Maradon, gwarzon gasar cin kofin duniya na Argentina kuma daya daga cikin mafi girma da ya taba buga wasan wanda ya mutu a Argentina a watan Nuwamba 2020 ya na da shekaru 60.

Kafin rasuwar Hugo an hango shi filin wasa na Maradona da ke Naples ta kasar Italiya, domin halartar bikin tunawa da dan uwansa marigayi kuma fitaccen dan wasan kwallon kafa wata daya kacal da ya wuce.

Kafin rasuwar sa ya dai bar mace mai suna Paola Morra, wadda ya aura a shekara ta 2016, tare da ’ya’ya uku.

Ƙananan ‘yan’uwan Maradona da sauran su ne Diego da Raul da Hugo shi ma dan wasan Æ™wallon Æ™afa ne kuma ya sanya hannu tun ya na matsayin matashi ga kungiyar Napoli mai shekaru 18 a 1987.

Amma ba kamar É—an’uwansa ba, wanda ya buga wasa mafi kyawun shekarunsa a Napoli kuma a na girmama shi a birnin Naples ta kasar Italiya a matsayin wani mutum mai daraja.
A ranar 20 ga Satumba, 1987, ‘yan’uwan biyu sun yi wasa da juna tare da Napoli wanda a ka buga 2-1.

Hugo, wanda ya kasance tauraron tawagar Argentina a gasar cin kofin matasa na duniya na FIFA na matasa ‘yan kasa da shekaru 16 a shekarar 1985, wanda ya kasance kan gaba a gasar cin kofin duniya na ‘yan kasa da shekaru 17, ya ci gaba da taka leda a kananun gasa na Spain da Austria da Venezuela kafin ya kawo karshen aikinsa na buga wasa a Japan a karshen shekarun 1990.

Bayan haka ya koma horarwa, kuma ya shiga cikin ajin manyan makarantun matasa a matsayin masu horaswa.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp