Gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar, ya ce, wajibi ne kafafen yada labarai na rediyo da talabijin su samarwa da kansu mafita, sakamakon yadda wasu kafafen sada zumunta ke yada labarai na kanzon kurege.
Badaru ya tabbatar da hakan ne yayin taron kaddamar da kwamitin kungiyar kafafen yada labara shiyar Arewa maso Yamma wanda ya gudana a ranar Laraba a Dutse.
Yayin taron shugaban kwamitin hukumar kula da kafafen yada labarai na jihar Jigawa, Alhaji Mati Ali, wanda ya kasance a matsayin mai saukar baki a taron, ya ja hankalin gidajen rediyo da talabijin da su kara zage damtse a kan ayyukan su.
Dr Bello Sule ya gabatar da mukala mai taken ”Kalubalen da kafafen yada labarai ke fuskanta daga kafafen sada zumunta tare da damar da a ke da ita’.
Ya ce”Babbar illar da ke tattare da harkar yada labarai a yanzu shi ne, marasa ilimi ne su ka dabaibaye harkar wanda ke amfani da kafafen sada zumunta na zamani wajen yada labarai da hotuna marasa tushe balle makama a cikin al’umma”.
Taron ya samu halartar shugabannin wasu kafafen gidajen rediyo da na talabijin da ke yankin Arewa maso Yamma.