fidelitybank

BON: Badaru ya gargadi gidajen rediyo da talabijin

Date:

Gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar, ya ce, wajibi ne kafafen yada labarai na rediyo da talabijin su samarwa da kansu mafita, sakamakon yadda wasu kafafen sada zumunta ke yada labarai na kanzon kurege.

Badaru ya tabbatar da hakan ne yayin taron kaddamar da kwamitin kungiyar kafafen yada labara shiyar Arewa maso Yamma wanda ya gudana a ranar Laraba a Dutse.

Yayin taron shugaban kwamitin hukumar kula da kafafen yada labarai na jihar Jigawa, Alhaji Mati Ali, wanda ya kasance a matsayin mai saukar baki a taron, ya ja hankalin gidajen rediyo da talabijin da su kara zage damtse a kan ayyukan su.

Dr Bello Sule ya gabatar da mukala mai taken ”Kalubalen da kafafen yada labarai ke fuskanta daga kafafen sada zumunta tare da damar da a ke da ita’.

Ya ce”Babbar illar da ke tattare da harkar yada labarai a yanzu shi ne, marasa ilimi ne su ka dabaibaye harkar wanda ke amfani da kafafen sada zumunta na zamani wajen yada labarai da hotuna marasa tushe balle makama a cikin al’umma”.

Taron ya samu halartar shugabannin wasu kafafen gidajen rediyo da na talabijin da ke yankin Arewa maso Yamma.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp