fidelitybank

Boko Haram sun kai hari tare da yin garkuwa da jami’an ‘yan sanda

Date:

‘Yan kungiyar ta’adda ta Boko Haram sun kai farmaki makarantar horas da ‘yan sanda ta Mobile da ke karamar hukumar Limankara Gwoza a jihar Borno, inda suka yi awon gaba da mutane da dama.

Kamar yadda jaridar Punch ta rawaito, masu garkuwan sun tafi da wasu ‘yan sandan na Mobile wadanda ba a tantance adadinsu ba.

Makarantar horarwa ta na kilomita ashirin da biyar daga garin Gwoza, mahaifar Sanata Ali Ndume, shugaban kwamitin majalisar dattawa akan sojoji. Gari ne mai iyaka tsakanin Borno da karamar hukumar Madagali ta jihar Adamawa.

Rahotanni sun ce mayakan ‘yan tada kayar bayan sun kai hari makarantar horon ne a daren ranar Alhamis da manyan bindigogi inda suka rinka harbin iska kafin su yi awon gaba da jami’i mai bayar da umarni.

Harin dai na zuwa ne kwanaki bakwai, bayan da ‘yan ta’addan suka yi yunkurin kutsawa cikin sansanin sojojin Najeriya da ke Gwoza inda wasu sojojin Najeriya suka yi nasarar fatattakar su.

Kwamitin Majalisar Dattawa kan Sojoji karkashin jagorancin Sanata Ali Ndume ya kai ziyarar aiki zuwa rundunar Operation Hadin Kai da ke yankin kwanaki biyu da suka gabata.

Har ila yau, Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, ya koka da yadda matsalar tsaro a jihar da kuma yankin Arewa maso Yamma ke ciki a halin yanzu, inda ya bukaci sojoji da su daina sassauta musu.

A cewar Zulum, ‘yan ta’addan Boko Haram a yanzu suna bukukuwan aure, suna karbar haraji daga wasu al’ummomi ba tare da wata arangama da sojoji ba.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp