‘Yan kungiyar ta’adda ta Boko Haram sun kai farmaki makarantar horas da ‘yan sanda ta Mobile da ke karamar hukumar Limankara Gwoza a jihar Borno, inda suka yi awon gaba da mutane da dama.
Kamar yadda jaridar Punch ta rawaito, masu garkuwan sun tafi da wasu ‘yan sandan na Mobile wadanda ba a tantance adadinsu ba.
Makarantar horarwa ta na kilomita ashirin da biyar daga garin Gwoza, mahaifar Sanata Ali Ndume, shugaban kwamitin majalisar dattawa akan sojoji. Gari ne mai iyaka tsakanin Borno da karamar hukumar Madagali ta jihar Adamawa.
Rahotanni sun ce mayakan ‘yan tada kayar bayan sun kai hari makarantar horon ne a daren ranar Alhamis da manyan bindigogi inda suka rinka harbin iska kafin su yi awon gaba da jami’i mai bayar da umarni.
Harin dai na zuwa ne kwanaki bakwai, bayan da ‘yan ta’addan suka yi yunkurin kutsawa cikin sansanin sojojin Najeriya da ke Gwoza inda wasu sojojin Najeriya suka yi nasarar fatattakar su.
Kwamitin Majalisar Dattawa kan Sojoji karkashin jagorancin Sanata Ali Ndume ya kai ziyarar aiki zuwa rundunar Operation Hadin Kai da ke yankin kwanaki biyu da suka gabata.
Har ila yau, Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, ya koka da yadda matsalar tsaro a jihar da kuma yankin Arewa maso Yamma ke ciki a halin yanzu, inda ya bukaci sojoji da su daina sassauta musu.
A cewar Zulum, ‘yan ta’addan Boko Haram a yanzu suna bukukuwan aure, suna karbar haraji daga wasu al’ummomi ba tare da wata arangama da sojoji ba.