Ofishin kula da basussuka na Najeriya (DMO) ya ce, ba ya cikin yarjejeniyar da Najeriya ta kulla da kasar Sin na cewa za ta jinginar da wasu kadarorinta ko da ta gaza biyan bashinta.
Babbar daraktar Ofishin, Misis Patience Oniha ce, ta sanar da hakan yayin tattaunawarta da kamfanin dillancin labarai na NAN a Abuja ranar Asabar.
A cewar ta,”Babu wata yarjejeniyar jinginar da wasu kadarorin gwamnatin Najeriya a cikin bashin, bashin da kasar Sin ke bin Najeriya bai wuce Dalar Amurka biliyan 3.59 ba, wanda ke zaman kaso 9.4 cikin 100 na Dala biliyan 37.9 din da ta ciyo daga ketare. Ya zuwa karshen watan Satumban 2021, jimlar bashin da ake bin Najeriya shi ne biliyan 37.9, wanda ya kunshi wanda gwamnatin tarayya da jihohi 36 da kuma babban birnin tarayya su ka ciyo daga ketare. Amma jimlar bashin da aka ciyo daga Sin bai wuce kaso 9.4 cikin 100 b, basussukan kuma ba sa bukatar wata jinginar kadara a matsayin sharadi, kawai yarjejeniya ce”. Inji Misis Patience.
A cikin ‘yan kwanakin nan ne dai a ka ta ce-ce-kuce a kafafen sada zumunta da na yada labarai cewa, wasu kasashen Afirka, ciki har da Najeriya na fuskantar barazanar karbe wasu muhimman kadarorinsu daga kasar Sin, saboda bashin da kasar ke bin su.