fidelitybank

Biyan Bashi: Babu batun sayar da kadarorin Najeriya – Ofishin Kula Bashi

Date:

Ofishin kula da basussuka na Najeriya (DMO) ya ce, ba ya cikin yarjejeniyar da Najeriya ta kulla da kasar Sin na cewa za ta jinginar da wasu kadarorinta ko da ta gaza biyan bashinta.

Babbar daraktar Ofishin, Misis Patience Oniha ce, ta sanar da hakan yayin tattaunawarta da kamfanin dillancin labarai na NAN a Abuja ranar Asabar.

A cewar ta,”Babu wata yarjejeniyar jinginar da wasu kadarorin gwamnatin Najeriya a cikin bashin, bashin da kasar Sin ke bin Najeriya bai wuce Dalar Amurka biliyan 3.59 ba, wanda ke zaman kaso 9.4 cikin 100 na Dala biliyan 37.9 din da ta ciyo daga ketare. Ya zuwa karshen watan Satumban 2021, jimlar bashin da ake bin Najeriya shi ne biliyan 37.9, wanda ya kunshi wanda gwamnatin tarayya da jihohi 36 da kuma babban birnin tarayya su ka ciyo daga ketare. Amma jimlar bashin da aka ciyo daga Sin bai wuce kaso 9.4 cikin 100 b, basussukan kuma ba sa bukatar wata jinginar kadara a matsayin sharadi, kawai yarjejeniya ce”. Inji Misis Patience.

A cikin ‘yan kwanakin nan ne dai a ka ta ce-ce-kuce a kafafen sada zumunta da na yada labarai cewa, wasu kasashen Afirka, ciki har da Najeriya na fuskantar barazanar karbe wasu muhimman kadarorinsu daga kasar Sin, saboda bashin da kasar ke bin su.

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...
X whatsapp