fidelitybank

Biyan Bashi: Babu batun sayar da kadarorin Najeriya – Ofishin Kula Bashi

Date:

Ofishin kula da basussuka na Najeriya (DMO) ya ce, ba ya cikin yarjejeniyar da Najeriya ta kulla da kasar Sin na cewa za ta jinginar da wasu kadarorinta ko da ta gaza biyan bashinta.

Babbar daraktar Ofishin, Misis Patience Oniha ce, ta sanar da hakan yayin tattaunawarta da kamfanin dillancin labarai na NAN a Abuja ranar Asabar.

A cewar ta,”Babu wata yarjejeniyar jinginar da wasu kadarorin gwamnatin Najeriya a cikin bashin, bashin da kasar Sin ke bin Najeriya bai wuce Dalar Amurka biliyan 3.59 ba, wanda ke zaman kaso 9.4 cikin 100 na Dala biliyan 37.9 din da ta ciyo daga ketare. Ya zuwa karshen watan Satumban 2021, jimlar bashin da ake bin Najeriya shi ne biliyan 37.9, wanda ya kunshi wanda gwamnatin tarayya da jihohi 36 da kuma babban birnin tarayya su ka ciyo daga ketare. Amma jimlar bashin da aka ciyo daga Sin bai wuce kaso 9.4 cikin 100 b, basussukan kuma ba sa bukatar wata jinginar kadara a matsayin sharadi, kawai yarjejeniya ce”. Inji Misis Patience.

A cikin ‘yan kwanakin nan ne dai a ka ta ce-ce-kuce a kafafen sada zumunta da na yada labarai cewa, wasu kasashen Afirka, ciki har da Najeriya na fuskantar barazanar karbe wasu muhimman kadarorinsu daga kasar Sin, saboda bashin da kasar ke bin su.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...
X whatsapp