Wani rahoto game da matsalar tsaro a Najeriya, ya ce satar mutane ya ƙaru a watan Nuwamba kaɗai a sassan Najeriya.
Rahoton ya kuma ce, an kashe mutum 404 a jihohi 28 na Najeriya a ƙananan hukumomi 115 a cikin watan Nuwamba kaɗai.
Kamfanin Beacon Consulting ya kuma ce, duk wata yakan fitar da rahoto kan binciken da ya yi game da matsalar tsaro a Najeriya tare da bayar da shawarwari ga mahukunta.
A cewar rahoton, satar mutane a Najeriya ta ƙaru da kusan kashi 38 a Nuwamba idan aka kwatanta da alƙalumman rahoton na watan Oktoba. Inji BBC