Wutar lantarki ta babbake wani mutum har lahira a lokacin da ya ke kokarin da ake zargin shi da satar wayar wutar transfoma a kauyen Lambu da ke karamar hukumar Tofa ta Jihar Kano.
Wani mazaunin garin mai suna, Naziru Lambu, shaidawa Aminiya cewa, abin ya faru ne da misalin karfe 1 na dare kafin wayewar garin Laraba.
Ya bayyana cewa wutar ta babbake mutumin ne bayan da ya gama kwance wayoyin har ya ajiye su a kusa da tranfomar.
Ya kuma ce, “Wasu ’yan garin sun ce, sun ji karar taratsatsin wutar lantarki a cikin dare da kuma ihun mutumin da ake kyautata zaton barawo ne kafin ya mutu”.
“An tsinci gawar mutumin ta na lilo, shi kuma ya rike waya a hannunsa”. In ji Naziru.
Tuni dai jami’an tsaro da na kamfanin wutar lantarki ta KEDCO suka isa kauyen Lambu, domin gudanar da bincike a kan abin da ya faru.