fidelitybank

Ban ga abinda zai dawo da ni siyasa ba — Obasanjo

Date:

 

Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo a ranar Asabar ya sake jaddada ƙudurinsa na ficewa daga harkokin siyasa, inda ya ce babu abin da zai sa ya koma harkar siyasar jam’iyya.

Obasanjo ya baiyana hakan ne a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai jim kadan bayan wata ganawar sirri da ‘yan Kwamitin Gudanarwa na Jam’iyyar PDP na ƙasa a Abeokuta.

Tsohon shugaban kasar ya ce ya gamsu da zama dattijon ƙasa, inda ya kara da cewa babu abin da zai sa ya koma siyasa.

“Ina so in jaddada cewa yanzu ba na cikin harkar siyasa kuma babu wani abu da zai dawo da ni siyasa.

“Zan kasance mai sha’awar abin da ke da kyau ga Najeriya kuma duk wanda ke son samun shawarata, zan ba shi musamman don amfanin Najeriya da kuma maslahar Afirka.

“Wannan shine dalilin da ya sa nake da irin nauyin da nake da shi a yanzu a Afirka, wanda ba abu ne mai sauki ba,” in ji tsohon shugaban.

Sai dai ya ce PDP za ta ci gaba da kasancewa cikin tarihin rayuwarsa saboda ya kai matsayin shugaban ƙasa a dandalin jam’iyyar.

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp