fidelitybank

Ballon d’Or: Ronaldo ya mayar da martani mai zafi a kan kyautar

Date:

Cristiano Ronaldo ya zargi editan kwallon kafa na Faransa da yin karya bayan ya ce burin dan kasar Portugal shi ne ya yi ritaya da karin kyautar Ballon d’Or fiye da Lionel Messi.

Mai shirya Ballon d’Or Pascal Ferre ne ya yi wannan ikirarin ga jaridar New York Times.

A ranar Litinin ne Messi na Paris St-Germain ya lashe kyautar Ballon d’Or karo na bakwai, yayin da Ronaldo wanda ya lashe sau biyar ya zo na shida.

Ronaldo ya ce “A ko da yaushe ina yin nasara ga kaina da kuma kungiyoyin da na ke wakilta. Na yi nasara ga kaina da kuma wadanda suke so na, ba na cin nasara a kan wani.”

A ranar Juma’a, Ferre ya shaida wa jaridar New York Times cewa: “Ronaldo ya na da buri daya kacal, kuma shi ne ya yi ritaya da karin Ballon d’Or fiye da Messi, kuma na san hakan saboda ya fada min”.

Ronaldo ya mayar da martani a shafukan sada zumunta inda ya ce, “Pascal Ferre ya yi karya, ya yi amfani da sunana wajen tallata kansa da kuma tallata littafin da ya ke yi wa aiki. Ba abin yarda ba ne cewa mutumin da ke da alhakin bayar da irin wannan babbar kyautar zai iya yin karya ta wannan hanyar, ba tare da mutunta wanda ya taba mutunta kwallon kafa ta Faransa Football da Ballon d’Or ba. Babban burina a rayuwata shi ne na lashe kofunan kasa da kasa a kungiyoyin da na ke wakilta da kuma ‘yan wasan kasa a kasata. Babban burina a rayuwata shine in bar sunana a rubuce a cikin haruffan zinare a tarihin kwallon kafa na duniya.” Inji Ronaldo.

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp