fidelitybank

Ballon d’Or: Ronaldo ya mayar da martani mai zafi a kan kyautar

Date:

Cristiano Ronaldo ya zargi editan kwallon kafa na Faransa da yin karya bayan ya ce burin dan kasar Portugal shi ne ya yi ritaya da karin kyautar Ballon d’Or fiye da Lionel Messi.

Mai shirya Ballon d’Or Pascal Ferre ne ya yi wannan ikirarin ga jaridar New York Times.

A ranar Litinin ne Messi na Paris St-Germain ya lashe kyautar Ballon d’Or karo na bakwai, yayin da Ronaldo wanda ya lashe sau biyar ya zo na shida.

Ronaldo ya ce “A ko da yaushe ina yin nasara ga kaina da kuma kungiyoyin da na ke wakilta. Na yi nasara ga kaina da kuma wadanda suke so na, ba na cin nasara a kan wani.”

A ranar Juma’a, Ferre ya shaida wa jaridar New York Times cewa: “Ronaldo ya na da buri daya kacal, kuma shi ne ya yi ritaya da karin Ballon d’Or fiye da Messi, kuma na san hakan saboda ya fada min”.

Ronaldo ya mayar da martani a shafukan sada zumunta inda ya ce, “Pascal Ferre ya yi karya, ya yi amfani da sunana wajen tallata kansa da kuma tallata littafin da ya ke yi wa aiki. Ba abin yarda ba ne cewa mutumin da ke da alhakin bayar da irin wannan babbar kyautar zai iya yin karya ta wannan hanyar, ba tare da mutunta wanda ya taba mutunta kwallon kafa ta Faransa Football da Ballon d’Or ba. Babban burina a rayuwata shi ne na lashe kofunan kasa da kasa a kungiyoyin da na ke wakilta da kuma ‘yan wasan kasa a kasata. Babban burina a rayuwata shine in bar sunana a rubuce a cikin haruffan zinare a tarihin kwallon kafa na duniya.” Inji Ronaldo.

assu update

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp