fidelitybank

Babu maganar sulhu ni da Ganduje – Kwankwaso

Date:

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya musanta batun tattaunawar sulhu da a ka ce ya na yi da Gwamnan Jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje.

Aminiya ta rawaito cewa, Kwankwaso ya bayyana haka ne cikin wata hira ta musamman da a ka yi da shi a gidan talabijin na Channels a ranar Lahadi, inda ya ce. ya ji dadin ziyarar ta’aziyyar da Gwamnan ya kai masa ta rasuwar kaninsa.

Sai dai ya kore yiwuwar bawa Ganduje damar samun wani matsayi ko mukami idan damar hakan ta samu ta bangarensa.

Ya ce “A yanzu dai ka san ba a jam’iyya daya mu ke ba, domin haka ina ganin babu ma bukatar yin wannan tambaya, domin haka ko da dama ta samu akwai mutanen da suka cancanta cikin wadanda na ke tare da su”.

A makon da ya wuce Kwankwaso ya musanta rade-radin da a ke na cewar ya na shirin ficewa daga jam’iyyar PDP tare da shirin sauya sheka zuwa APC, wanda hakan ya zama batun tattaunawa na tsawon lokaci a kafafen watsa labarai.

Rikicin Kwankwaso da Ganduje ya yi tsamari tun bayan 2015 bayan Gwamnan Kano na yanzu ya dare kan kujerar mulkin Jihar.

Sai dai a baya-bayan Ganduje ya nuna cewar akwai yiwuwar yin sulhu da tsohon uban gidan nasa a siyasa, wanda ya ce tun asali wasu ne suka shiga tsakaninsu.

Gwamna Ganduje na ci gaba da fuskantar rikicin cikin gida a jam’iyyarsu ta APC tsakaninsa da tsagin tawagar tsohon Gwamna kuma Sanatan Kano ta tsakiya a yanzu, Malam Ibrahim Shekarau.

Wanda a ke rikicin shugabancin jam’iyya tsakanin, Abdullahi Abbas da Haruna Abdullahi Zago.

 

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp