fidelitybank

Babu maganar sulhu ni da Ganduje – Kwankwaso

Date:

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya musanta batun tattaunawar sulhu da a ka ce ya na yi da Gwamnan Jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje.

Aminiya ta rawaito cewa, Kwankwaso ya bayyana haka ne cikin wata hira ta musamman da a ka yi da shi a gidan talabijin na Channels a ranar Lahadi, inda ya ce. ya ji dadin ziyarar ta’aziyyar da Gwamnan ya kai masa ta rasuwar kaninsa.

Sai dai ya kore yiwuwar bawa Ganduje damar samun wani matsayi ko mukami idan damar hakan ta samu ta bangarensa.

Ya ce “A yanzu dai ka san ba a jam’iyya daya mu ke ba, domin haka ina ganin babu ma bukatar yin wannan tambaya, domin haka ko da dama ta samu akwai mutanen da suka cancanta cikin wadanda na ke tare da su”.

A makon da ya wuce Kwankwaso ya musanta rade-radin da a ke na cewar ya na shirin ficewa daga jam’iyyar PDP tare da shirin sauya sheka zuwa APC, wanda hakan ya zama batun tattaunawa na tsawon lokaci a kafafen watsa labarai.

Rikicin Kwankwaso da Ganduje ya yi tsamari tun bayan 2015 bayan Gwamnan Kano na yanzu ya dare kan kujerar mulkin Jihar.

Sai dai a baya-bayan Ganduje ya nuna cewar akwai yiwuwar yin sulhu da tsohon uban gidan nasa a siyasa, wanda ya ce tun asali wasu ne suka shiga tsakaninsu.

Gwamna Ganduje na ci gaba da fuskantar rikicin cikin gida a jam’iyyarsu ta APC tsakaninsa da tsagin tawagar tsohon Gwamna kuma Sanatan Kano ta tsakiya a yanzu, Malam Ibrahim Shekarau.

Wanda a ke rikicin shugabancin jam’iyya tsakanin, Abdullahi Abbas da Haruna Abdullahi Zago.

 

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp