Sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya ya bayyana rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta na zamani cewa shi da Sanata Abdu Kwari sun dauki nauyin kudirin dokar sauya sunan Kaduna zuwa jihar Zazzau, a matsayin karya da ta wuce tunanin dan Adam.
Wani rahoto da kafafen yada labarai ke yadawa ya nuna cewa, Sanatocin biyu daga jihar Kaduna ne suka dauki nauyin kudirin canza sunan Kaduna zuwa jihar Zazzau.
Sanata Uba Sani, yayin da yake karyata rahoton, ya ce karya ne.
A cikin wata sanarwa a ranar Litinin, ya bayyana rahotannin a matsayin rashin gaskiya da karya.
A cewarsa, labarin karya ne na wasu bata gari da ke son kawo rudani a jihar Kaduna ke yada shi.