Fadar shugaban kasa, ta musanta rade-radin da ke nuni da cewa shugaban kasa, Muhammadu Buhari ne ya ba da umarnin korar hukumar gudanarwar kamfanin rarraba hasken lantarki na Abuja (AEDC).
Babban hadimin Shugaban kan harkokin yada labarai, Malam Garba Shehu ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwar da ya fitar, ya ce, zargin ba shi da tushe ballantana makama, kasancewar tun shekarar 2013 da gwamnati ta cefanar da harkokin lantarki, kuma kamfanin ya koma hannun ’yan kasuwa.
Sanarwar ta ce sam ba Buhari ne ya umarci a kori shugabannin ba, kuma ba shi da hannu a ciki, domin ba ya katsalandan a harkokin kamfanoni masu zaman kansu.