Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban birnin ƙasar, Abuja, inda ta yi kira ga mazauna birnin su cigaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum cikin lumana.
Gwamnatin Najeriya ta bayyana haka ne a matsayin martani ga gargaɗin tsaro da Amurka ta aika zuwa ga ƴanƙasarta da ke birnin Abuja.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Ministan Watsa Labarai na Najeriya, Mohammed Idris ya fitar, inda a ciki ya ce, “gwamnatin Najeriya ta samu labarin gargaɗin da Amurka ta aika wa ma’aikatan ofishin jakadancinta da ma ƴanƙasarta da ke Abuja game da tsaro.
“Duk da gwamnatin Najeriya na girmama haƙƙin da ofisoshin jakadanci – ciki har da na Amurka – ke da shi na ba ƴanƙasarta shawara ko gargaɗi game da matsalolin tsaro, yana da muhimmanci mu tabbatar da cewa babu wata barazanar tsaro da Najeriya ke fuskanta, sannan mazauna birnin da masu ziyara babu wata barazana da suke fuskanta.”
Sanarwar ta ƙara da cewa akwai cikakken tsaro a Abuja, “domin jami’an tsaro suna aiki ba dare ba rana domin tabbatar da daƙile dukkan wata barazanar tsaro.”