Mamali a jami’ar jiha ta Kaduna (KASU), Farfesa Mohammed Abubakar, ya yanke jiki yya fadi a cikin jami’ar, inda tuni ya rigamu gidan gaskiya.
Farfesa Mohammed Abubakar, wanda ya ke a fannin sabanta makamashi da ilimin kimiyyar kwayoyin halitta, a Jamiāar Jihar Kaduna (KASU), ya rasu ya na da shekaru 67 a duniya.
Har zuwa rasuwarsa a ranar Jumaāa da rana, Farfesa Abubakar ya kasance malami a sashin ilimin kimiya na KASU.
Da yake tabbatar da rasuwarsa ga Aminiya kanensa, Abdulrazak Abubakar, ya ce, marigayin ya fadi ne a jami’ar ta KASU da yammacin ranar Jumaāa, kuma aka garzaya da shi asibitin makarantar inda aka tabbatar da rasuwarsa.
Ya ce marigayi Farfesan wanda aka yi janaāizarsa kamar yadda addinin Musulunci ya tanada, ya kai āyaāyansa makaranta a safiyar ranar Jumaāa kafin ya dawo gida ya shirya aiki.
Marigayin ya rasu ya bar mata biyu da āyaāya 10 da jikoki.