Chiemeka Arinze, wanda ake tuhuma tare da hamshakin attajirin nan mai garkuwa da mutane, Chukwudi Dumee Onuamadike, wanda aka fi sani da Evans, ya mutu a gidan ajiya da gyara hali na Kirikiri.
Evans na fuskantar shari’a tare da Joseph Emeka, Arinze da Udeme Upong, kan yunkurin yin garkuwa da Cif Vincent Obianodo, Shugaban Kamfaninmotoci na Young Shall Grow Motors, a gaban Mai Shari’a Oluwatoyin Taiwo na wata Kotun Laifuka ta musamman da ke Ikeja a Legas.
A na tuhumar su da tuhume-tuhume Bakwai da suka hada da kisan kai, yunkurin kisan kai, hada baki domin yin garkuwa da mutane, yunkurin yin garkuwa da mutane da sayarwa da kuma musayar makamai.
Evans, wanda aka kama a watan Yunin shekarar 2017, jami’an tsaron Najeriya sun bayyana shi a matsayin mutum mai wayo, kuma haziki mai garkuwa da mutane da ya kaucewa kama shi tsawon shekaru Hudu, duk da cewa ya na cikin jerin wadanda ake nema ruwa a jallo a jihohi Uku ciki akwai jihar Legas da Edo da kuma Anambra.