Mahaifin Hanifa Abubakar da wani malamin makarantarta ya yi garkuwa da ita kuma ya yi mata kisan gilla, ya yi magana kan lamarin.
Mahaifin Abubakar wanda ya yi kuka sosai a lokacin da yake zantawa da manema labarai, ya ce, lamarin ne da ba za a taba mantawa da ita ba har sai ya mutu.
Ko da yake ya yarda cewa, kowane mai rai sai ya dandana mutuwa, mahaifin cikin raÉ—aÉ—i ya ce, “WaÉ—anda suka yi sanadiyar mutuwar diyarsa ba su yi mata adalci ba”.
Ya ce: “Gaskiya ina baƙin cikin abin da ya faru. Ina iya godewa Allah kawai. Wannan zai iya faruwa ga kowa, kuma a ce duk wanda ya rayu a yau zai mutu wata rana, domin haka na bar wa Allah komai, amma har na mutu ba zan manta da wannan ba.
“WaÉ—anda suka yi mini haka ba su yi mini adalci ba, haka kuma ba su yi wa duniya adalci ba. ‘Yata ta dawo daga makarantar Al-Qur’ani aka yi mata wannan abun, ba komai Allah ne zai bi min haki na”.
“Ina kuma gode wa jami’an tsaron Najeriya, musamman wadanda kokarinsu ya gano ‘yata da aka kashe.
“Allah ya bi mana hakkinmu, Allah kwato mana hakin ‘yar mu”. A cewar Abubakar