Wani mamba a kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, Alhaji Adamu Waziri, ya gargadi masu zabe da ’yan takara cewa babu inda za a yi magudi a zaben 2023 mai zuwa.
Waziri ya yi wannan gargadin ne a ranar Juma’a, 4 ga watan Nuwamba, 2022, a lokacin yakin neman zaben gwamna na jam’iyyar PDP a Nguru, jihar Yobe.
Tsohon ministan harkokin ‘yan sandan ya kuma yi amfani da dandalin wajen baiwa magoya bayan jam’iyyar da masu biyayya ga zabar masu gaskiya da rikon amana da za su ceto Najeriya daga yunwa da tabarbarewar tattalin arziki.
Waziri ya bayyana fatansa cewa jam’iyyar za ta yi nasara a dukkan matakai a zabukan.
“Tare da goyon bayan ku, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar da duk sauran ‘yan takara za su lashe zaben 2023,” in ji shi.
Hakazalika dan jam’iyyar PDP, ya yi kira ga masu zabe da su yi imani da jam’iyyar su fito gaba daya domin kada kuri’unsu.
Shima da yake jawabi, dan takarar gwamna na jam’iyyar a jihar Yobe, Alhaji Sheriff Abdullahi, ya yi alkawarin samar da ingantacciyar shugabanci idan aka zabe shi. Ya kuma bada tabbacin inganta albashin ma’aikatan jihar.
Taron ya samu halartar daruruwan magoya bayan jam’iyyar da masu biyayya da kuma sarakuna daga kananan hukumomi 17 na jihar.
A baya dai jam’iyyar PDP ta kaddamar da kwamitin yakin neman zaben ta na jiha (SCC) a ranar Talata 1 ga watan Nuwamba a Damaturu.