Gamayyar kungiyoyin da ke goyon bayan jam’iyyar APC ta Kudu maso Kudu, sun sha alwashin ba za su bari abin da ya faru a zabukan 2015 da 2019 ba, inda mutanen shiyyar ba su zabi jam’iyyar APC ba, ta sake maimaita kanta a zaben 2023.
Kungiyoyin sun kuduri aniyar fara wayar da kan jama’a tare da yakin neman zabe a unguwanni da sassan dake shiyyar, domin ganin dan takararsu na shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya fito, da kuma sauran ‘yan takarar jam’iyyar a jihar a zaben 2023.
Shugaban gamayyar kungiyar reshen jihar Akwa Ibom, Rt Hon Patty Etete Inemeh ne ya bayyana hakan a karshen mako a yayin gangamin yakin neman zabe na jam’iyyar APC ta Kudu a Uyo babban birnin jihar.
Inemeh ya bukaci kungiyoyin goyon bayan da su tashi tsaye wajen gudanar da gangami da wayar da kan jama’a a unguwanni da sassan fadin jihar domin jama’a a matakin kasa su samu kwarin guiwar zabar dukkan ‘yan takarar jam’iyyar APC, kamar yadda ya yaba da kyawawan halaye na dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC. Ahmed Tinubu.